'Yanbindiga sun sace mutum 117 da hallaka wasu tara a Jihar Kebbi
Sa'o'i 3 da suka wuce
Wasu 'yanbindiga sun hallaka akalla mutum tara sannan kuma suka yi awon-gaba da wasu magidanta 117, a garin Danmuntari da ke yankin Danko-Wasagu a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Wasu mazauna garin da suka tsira daga harin sun tabbatar wa da BBC, da cewa lamarin ya faru ne a yammacin ranar Talata, 27 ga watan Mayun, 2025, lokacin da 'yanbindigan su ka yi wa garin kofar-rago.
Daga cikin wadanda barayin dajin suka kashe har da wata mata mai jego da jaririnta, inda suka harbe su tare da sauran jama'ar da suka hallaka ta hanyar harbin kan-mai-uwa-da-wabi a lokacin da suka shiga garin, kamar yadda shedun suka yi bayani.
''Da la'asar barayin suka kewaye garin suka dinga harbe-harbe wanda hakan ya sa dole mutanen garin suka watse suka cimma na kashewa, suka kashe mutum tara,''in ji daya daga cikin mutanen garin.
Comments
Post a Comment